Hakan ya biyo bayan wata doka ce da shugaba Abdel Fattah Al-Sisi ya zartar, wacce ta bada damar a gurfanar da fararen hula da ake zargi da kai hare-hare kan dukiyar gwamnati, a gaban kotunan soji.
Kungiyoyin kare hakkin dan Adam sun yi Allah wadai da matakin gurfanar da fararen hula a gaban kotuna soji, inda suka ce babu adalci a kotunan.
Kawo yanzu dai, fiye da magoya bayan hambararren shugaba Morsi dubu 15 ne ke daure a gidajen yari a kasar tun bayan da aka hambarar da shi a watan Yulin bara.
Wasu daruruwa daga cikinsu, hukuncin kisa aka yanke musu.ABNA